Dan takarar gwamnan jihar Kano ƙarƙashin jam’iyyar ADP sha’aban Ibrahim Sharada ya faɗa Aa taron muhawarar ‘yan takarar gwamna da BBC ta gabatar cewa zai gayyato manyan-manyan ‘yan kasuwa don su zo su zuba jari a jihar Kano domin bunƙasa harkokin kasuwancin jihar.
Ya kuma ƙara da cewa zai baiwa karananna hukumomin gashin kansu, tare da inganta masana’antun jihar da ke Bomfai da Chalawa.
”Za mu janyo manyan ‘yan kasuwa na ƙasashen wajen domin su zo Kano su haɗu da ‘yan kasuwarmu tare da haɓaka kasuwanci a jihar” in ji Sha’aban
Da aka tambaye shi cewa baya ganin matsalar tsaron da ƙasar ke fusknata zai kawo cikas ga zuwamn masu zuba jarin daga ƙasashen waje?
Sai Sha’aban ya ce, zai gina kyakkayawar alaƙa da ƙasashen waje domin ba su damar zuwa ƙasar.
Ya kuma sha alwashin habaka kuɗin shigar jihar daga biliyan 2.5 zuwa biliyan goma a kowanne wata.