Emmanuel Macron ya tabbatar da cewa, zai yi kokarin hada kan Faransa bayan an sake zabarsa a matsayin shugaban kasa a karo na biyu.
A jawabinsa na nasarar da ya yi ga taron jama’ar da suka taru a hasumiyar Eiffel da ke birnin Paris, ya amince da cewa mutane da dama sun kaurace wa ko kuma sun zabe shi ne kawai don hana abokiyar hamayyar sa Marine Le Pen mai tsatsauran ra’ayi shiga fadar Elysee.
Mista Macron, wanda ya zamo shugaban Faransa na farko da aka zaba a wa’adi na biyu cikin shekaru ashirin, ya yi alkawarin samar da sabbin tsare-tsare, tare da mayar da hankali kan matasa da muhalli, ya kara da cewa ba za a bar kowa a baya ba.
Tazarar da Mista Macron ya samu a zaben na ranar Lahadi ta kai kashi goma sha bakwai bisa dari kan abokiyar hamayyarsa.