fidelitybank

Zan gwangwaje Matar da ta ci ciyawa a hannun ƴan bindiga – Gwamnan Zamfara

Date:

Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara, ya karɓi wata dattijuwa wadda ƴan bindiga suka sace da kuma bidiyonta ya karaɗe shafukan sada zumunta.

Bidiyon dai ya nuna wata uwa da ‘ya’yanta a hannun ƴan bindiga, waɗanda har suka koma cin ciyawa. Sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar, na cewa ganin halin da matar ta shiga, ya zama tilas a tashi haikan wajen shawo kan matsalar ta ƴan fashin daji da kuma tabbatar da cewa iyalai sun samu ababen more rayuwa.

Sanarwar ta ce gwamnan ya karɓi matar ne domin hakan na cikin zimmarsa ta ganin an kare rayuka da ma dukiyoyin al’ummar Zamfara.

“Gwamna Lawal ya karɓi Hauwa’u Salisu, matar da ta rasa komai saboda rikicin ƴan fashin daji.

Ya nuna zimmarsa ta ganin an kawo karshen matsalar tsaro a Zamfara, sannan ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan da ayyukan ƴan bindiga ya daidaita,” in ji sanarwar.

Gwamnan ya bai wa matar wani sabon gida da za ta zauna da ‘ya’yanta. Ya kuma tabbatar wa matar cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da ciyar da ‘ya’yanta da kuma samar musu abubuwan da suke buƙata.

Har ila yau, gwamnan ya bayar da umarnin cewa a gaggauta sanya yaran matar a makaranta da kuma ba su cikakken tallafin karatu.

Ya kuma buƙaci dukkan hukumomi su yi ƙoƙari wajen binciko iyalai marasa galihu da ke fuskantar irin waɗannan matsaloli, don ganin cewa an ba su taimakon da ya kamata

punch newspaper headlines today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp