fidelitybank

Zan gudanar da gwamnatin da al’umma za su ji dadin ta – Abba Kabir

Date:

Sabon zaɓaɓɓen gwamnan jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP, ya ce, zai gudanar da gwamnatin da za ta fifita maslahar al’umma da kuma kyautata ilimi.

A jiya ne hukumar zaɓe mai zaman kanta ta INEC ta bayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar da aka gudanar da ranar asabar din da wuce.

A tattaunawarsa da BBC Abba Kabira ya ce al’umar jihar sun nuna masu ƙauna a lokacin da yake ya ƙin neman zaɓe da kuma a ranar zaɓe, kan haka ne ma ya ce bai yi mmaki ba da hukumar INEC ta bayyana shi a matsayin wanda ya yi nasara a zaɓen.

Ya ƙara da cewa ba zai yi sako-sako wajen yaƙi da cin hanci da kyautata rayuwar al’umma ba.

Sabon zaɓaɓɓen gwamnan na Kano ya ce zai bayar da fifiko wajen kyautata ilimi da lafiya da kasuwanci da tsaro da harkokin noma.

Abba Gida-gida ya ce cikin kwanaki 100 na farkon mulkinsa zai yi kokarin kyautata ɓangaren ilimin jihar.

Abba Gida-gida – wanda tsohon kwamishinan ayyukan ne zamanin mulkin tsohon gwaman jihar Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso – ya alƙawarta cewa zai ƙarasa duk ayyukan da gwamnatin jihar ta yanzu ta faro matuƙar za su amfanar da al’ummar jihar.

Sabon gwamnan ya lashe zaɓen da aka gudanar da ƙuri’u miliyan 1,019,602, bayan doke babban abokin hamayyarsa mataimakin gwamnan jihar Nasiru Gawuna na jam’iyyar APC mai mulkin jihar, wanda ya samu ƙuri’u 890,705.

sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp