Gwamnan jihar River Ben Ayade ya ce, babban jagoran APC mai mulki, Bola Ahmed Tinubu, ya na da damar da zai nemi kujerar shugaban kasa.
A wata hira da ya yi da BBC, Farfesa Ben Ayade ya bayyana cewa, la’akari da wahalar da Bola Ahmed Tinubu ya sha da APC, babu laifi don ya fito ya bayyana muradinsa.
Farfesa Ayade, ya ce, tsohon gwamna Tinubu ya yi yaki wajen ganin an kafa gwamnatin Muhammadu Buhari, wanda a ka kifar da PDP shekaru kimanin bakwai da suka shafe.
A cewar Gwamna Ayade, “Muddin jam’iyyar APC ta ce a marawa Bola Tinubu baya, zai goyi bayan sa, tun da ya yi bauta, ba zai yi wu ayi masa dare a zabe mai zuwa ba. Duk wanda zai fito takara daga yankin kudancin Najeriya, ya fito. Za ma a samu karin wadanda za su nemi takara. Idan ka tambaye ni game da Bola Tinubu, zan ce ya yi daidai da ya fito takara, dalili kuwa shi ne ya yi wa Buhari kokari.”