fidelitybank

Zan farfado da tattalin arziki da maganin ‘yan ta’adda – Tinubu

Date:

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Asiwaju Ahmed Bola Tinubu, ya bayar da tabbacin cewa, idan aka zabe shi a kan mulki a zaben shugaban kasa na 2023, zai yi yaki da tada kayar baya da rashin aikin yi.

Tinubu ya bayyana hakan ne yayin wani gagarumin gangami da aka gudanar a jihar Kaduna wanda ya samu halartar dubban magoya bayan jam’iyyar APC daga shiyyar arewa maso yammacin kasar nan.

Taron ya gudana ne na shugaban kasa, Gwamna, Sanata, ‘yan takarar Majalisar Wakilai da na Jiha a shiyyar Arewa maso Yamma da ta kunshi jihohin Kaduna, Kano, Kebbi, Jigawa Katsina, Sokoto da Zamfara.

Tinubu ya kuma bayyana cewa, za a samar da ayyukan yi ga matasa masu yawan gaske a fadin kasar nan, inda ya ce zai farfado da noma domin samar da abinci.

“Da wadannan, ‘yan Najeriya za su samu kwanciyar hankali saboda za a samu wadatar abinci a kasar,” in ji shi.

Yayin da yake jawabi ga magoya bayan da suka fito daga shiyyar Arewa maso Yamma, Tinubu ya ce bai ji dadin rashin tsaro a jihar Kaduna musamman da ma Najeriya baki daya ba.

Ya kuma yabawa Gwamna Nasir El-Rufa’i bisa yadda jihar ke ci gaba da bunkasa ababen more rayuwa, inda ya nuna gamsuwa da sanin cewa Gwamnan yana da gogaggen mutum da zai karbi ragamar mulki daga hannun shi Uba Sani, dan takarar gwamna na jam’iyyar a jihar. .

“Dukkan masu tayar da hankali, masu garkuwa da mutane, masu kashe mutane da ke damun tsaro a Kaduna da Arewacin Najeriya, ina tabbatar muku, za mu kawar da su.

“El-Rufai ya ajiye gado a jihar Kaduna kuma ya bunkasa kudaden shiga da ake samu a cikin gida. Amma shugaban da ba shi da magajin kwarai ba shugaba ne nagari ba,” inji shi.

“Uba Sani matashi ne, mai kuzari kuma mai gaskiya, kuma yakamata ya zama gwamnan jihar Kaduna.

Ya kara da cewa, “Ya kamata ku zabi dukkan ‘yan takarar APC, a kowane mukami na zabe.”
Da yake jawabi tun da farko, shugaban jam’iyyar na kasa, Abdullahi Adamu, ya bayyana jin dadinsa ga al’ummar jihar bisa yadda suka fito domin karbar dan takararsu na shugaban kasa.

Daga cikin manyan baki da suka halarci gangamin akwai Gwamna Nasir El-Rufai na jihar Kaduna, Abubakar Badaru na Jigawa, Atiku Bagudu na Kebbi, Simon Lalong na Filato, Aminu Masari na Katsina, da Bello Mohammed Mattawalle na jihar Zamfara.

www.nigeriannewspapers.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnan Kano ya kori mataimansa na musamman kan belin Danwawu

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da...

Tsohon Minista a mulkin Buhari ya mutu

Allah ya yi wa tsohon ministan noma da raya...

Kashi 70 na yankin Bukuyum ta Kudu na Ĉ™arĈ™ashin Ĉ´an Bindiga – ĈŠan majalisa

Rahotanni daga yakin Ĉ™aramar hukummar Bukuyum na jihar Zamfara...

Goodluck ya fi dacewa ya zama dan takara a 2027 – Lamido

Tsohon Gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido ya ce Tsohon...

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin Ĉ™asa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ĉ³ansanda

Kwamishinan Ĉ´ansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa Ĉ™uri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

ĈŠaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

AĈ™alla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aĈ™alla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...
X whatsapp