Sace-sace da kwacen waya su ne manyan kalubalen tsaro da ake fuskanta a Kano kuma za mu yi maganinsu, a cewar ɗan takarar gwamnan jihar Kano ƙarƙashin jam’iyyar PRP Salihu Tanko Yakasai.
Ya ce ya rasa aikinsa sabo da matsalar tsaron da ƙasar ke fuskanta, a yayin da yake magana a zauren taron muhawar ‘yan takarar gwamnan jihar Kano da BBC ta gudanar ranar Asabar.
Ya ƙara da cewa ”maganar sace-sacen waya wannan babbar matsala ce”, kuma gwamnati mai ci ta ɗauki matakin dakatar da matsalar ta hanyar hana ‘yan adaidaita fita tun daga ƙarfe goman dare, sai dai hakan na haifar da wata matsalar a cewarsa.
Sai dai ya ce, zai ɗauki matakin da ya dace domin dakatar da sace-sace da ƙwacen wayoyin ba tare da haifar da wata matsalar ba.
Sannan ya ce zai ɗauki matakin inganta tsaro tun daga unguwanni zuwa mazaɓu, domin inganta tsaro a faɗin jihar.