Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin tabbatar da cewa makiyan Shugaba Bola Tinubu za su cigaba ba da kamu da cutar hawan jini.
Wike ya ce ya gane cewa abokan hamayyar Tinubu ba su ji dadin kyawawan ayyukan da ya yi tun hawansa mulki a 2023 ba.
Ministan ya bayyana haka ne a lokacin kaddamar da titin Arterial Road N16 (Shehu Shagari Way) daga Ring Road 1 (Nnamdi Azikiwe Way) zuwa Arterial Road N20 (Wole Soyinka Way), tare da sauran hanyoyin da ke gundumar Katampe, babban birnin kasar, da Shugaba Tinubu ya yi a ranar Laraba.
Wike ya tuna yadda ya fahimci, yayin da yake kallon talabijin, cewa wasu mutane suna nuna bacin rai ga Tinubu.
Ministan ya sha alwashin ci gaba da kaddamar da ayyuka na yabawa wadanda za su kara tayar da hankali ga masu sukar Shugaban.
Ya ce: “A wasu lokatai, ban sani ba, a ruhaniya ana taɓa ni. Sai kawai aka taɓa ni don kunna ta (TV) kuma ina kallo, kuma ban fahimci cewa mutane za su iya jin zafi ba, amma yanzu na san cewa irin waɗannan mutane suna jin zafi.
“Yanzu dole ne in tabbatar da cewa na ci gaba da ba su hawan jini, yayin da suke ci gaba da jin zafi, zai yi mana dadi, kuma yanzu aikina ne.
“Zan yi farin ciki, ina zagawa, da dariya a kowane lokaci, kuma za su kasance a can suna ihu, fada, da kashe kansu. Don haka, shugaban kasa, na gode da kasancewa cikin wannan juyin juya hali.”