A ranar Juma’ar da ta gabata ne shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ba da tabbacin cewa, gwamnatin tarayya za ta ci gaba da zage damtse wajen ganin an dawo da kayayyakin tarihi na Najeriya da aka sace daga kasashen waje da suka hada da Tagulla 1,130 na Benin Bronzes a cikin gidajen tarihi na kasar Jamus.
Shugaban ya bayar da wannan tabbacin ne a lokacin da ya karbi bakuncin Oba na Benin, Oba Ewuare II, tare da rakiyar mambobin kotunan masarautar Benin da kwamitin amintattu na gidan adana kayan tarihi na Benin a fadar shugaban kasa da ke Abuja.
Mai Martaba Sarkin ya ziyarci fadar shugaban kasa ne, domin mika godiyarsa ga shugaban kasar kan komawar wasu muhimman tagulla biyu na kasar Benin kwanan nan da jami’ar Cambridge da ta Aberdeen da ke kasar Burtaniya suka yi, bayan shekaru 125 da suka gabata.
Da yake jawabi a kan dawo da kayayyakin tarihi, shugaba Buhari ya bayyana jin dadinsa da yadda ya kawo farin jini ga Najeriya da tsohuwar masarautar Benin da kuma farin ciki ga Oba na Benin.