fidelitybank

Zan ci gaba da aiki na – Chris Ngige

Date:

Ministan Ƙwadago a Najeriya Chris Ngige ya janye daga neman takarar shugaban ƙasa da yake yi ƙarƙashin jam’iyya mai mulki ta APC, yana mai cewa zai ci gaba da aikinsa na minista.

Da yake bayyana janyewar tasa a cikin wata sanarwa ranar Juma’a a Abuja, Mista Ngige ya ce ya ɗauki matakin ne bisa kishin Najeriya.

“Na ɗauki matakin bisa kishin ƙasa don na samu damar mayar da hankali kan aikina na ci gaba da taimaka wa Shugaban Ƙasa da gwamnati…kuma da dalilai na iyalaina,” in ji sanarwar.

Ministan ya ƙara da cewa zai ƙaurace wa “shiga duk wasu shirye-shiryen APC na zaɓen 2023 tun daga kan zaɓukan fid da gwani”.

Ya ce tuni ya faɗa wa shugaban ƙasa matakin da ya ɗauka.

A jiya Juma’a ne Shugaba Buhari ya yi wa ministocinsa 10 ban-kwana da ke son tsayawa takara a muƙamai daban-daban, kuma Ngige na cikinsu. In ji BBC.

daily post today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp