Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabiu Kwankwaso, ya sayi fom ɗin takarar Jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) na zaɓen shugaban ƙasa a 2023.
Kwankwanso, wanda ya samu fom din nuna sha’awar jam’iyyar NNPP a jiya, ya bukaci ‘yan Najeriya musamman ‘yan siyasa da su shiga jam’iyyarsa, domin ceto Najeriya daga talauci, rashin aikin yi da rashin tsaro.
‘Wannan jam’iyya ce mai ci gaba mai son sauya yanayin siyasar kasar nan. Idan ka je kowace unguwa a yanzu, jam’iyyar da mutane ke magana a kai yanzu ita ce NNPP. Masu son bunkasa kasar nan su shiga NNPP,” inji shi.