Ɗan takarar gwamnan jihar Kano, ƙarƙashin inuwar jam’iyyar NNPP, Abba Kabkir Yusuf, ya ce, babban abin da gwamnatinsa za ta sanya a gaba shi ne bayar da ilimi kyauta ga ‘yan asalin jihar.
Abba kabir ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi a taron muhawar ‘yan takarar gwamna da BBC ta shirya a jihar ranar Asabar.
A lokacin da mai gabatar da muhawar ya tambaye shi cewa ta ina zai samo kuɗin da zai bayar da ilimi kyauta a jihar a daidai lokacin da jihohi da dama ke kokawa kan matsin tattalin arziki?
Sai Abba Kabir ya ce ”Idan ka dakile cin hanci da rashawa a Kano to ka yi maganin matsalar”.
Sannan ya ce zai bunƙasa hanyoyin samun kuɗin shiga ta hanyar nemo taimako a wajen ƙungiyoyin bayar da tallafi domin tallafa wa ilimi a jihar.
Abba Kabir ya kuma ce zai mayar da hankali wajen ɗaukar isassun malaman makaranta domin wadata jihar da malaman da take buƙata.