fidelitybank

Zan baiwa masu yi wa ƙasa hidima 1,215 dubu 30 kowanne su – Zulum

Date:

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya ce zai raba wa matasan da ke yi wa ƙasa hidima a jihar su 1,215 tallafin 30,000 kowanensu domin rage raɗaɗi.

Zulum ya bayyana haka ne lokacin da ya ziyarci sansanin horar da masu yi wa ƙasar hidima ranar Asabar a Maiduguri, inda ya ce zai ware naira miliyan 36.4 domin bai wa matasan tallafin.

Haka kuma gwamnan ya bai wa masu yi wa ƙasar hidima buhun shinkafa 100 da na wake 10 da jarkar man girki 10 domin yi wa matasan abinci a lokacin da suke karɓar horon na mako uku

“Ina son faɗaɗa rabon tallafin rage raɗadi ga masu yi wa ƙasarmu hidima da ke jiharmu. kowane mutum guda a cikinsu zai samu naira 30,000, za kuma a tura muku kudin ne ta asusun ajiyarku na banki”, in ji Zulum.

Ya kuma buƙaci matasan da su yi biyayya ga dokokin sansanin wajen zama lafiya tare da aiwatar da duka ayyukan da suka wajaba a kansu, domin ciyar da ƙasarsu gaba.

Gwamnan ya kuma bayyana jin dadinsa ga gwamnatin tarayyar ƙasar wadda ta inganta tsaron jihar domin bayar da dama da matasan domin su yi hidimar ƙasa a jihar.

An dai kwashe shekaru masu yawa ba tare da horar da masu yi wa ƙasaa hidima ajihar ba, sakamakon hare-haren ƙungiyar Boko Haram.

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp