fidelitybank

Zan baiwa jihohi dama su samar da wutar lantarki su -Atiku

Date:

Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya bayyana matakan da zai dauka wajen magance matsalar wutar lantarki da ta ki ci ta ki cinyewa a kasar.

Atiku Abubakar ya bayyana haka ne a wata sanarwar da ya fitar ranar Alhamis a Abuja babban birnin kasar.

Ya ce, abu na farko da zai yi idan ya hau mulki shi ne zai cire damar da gwamnatin tarayya ce kadai ke da ita ta samar da wutar lantarki ya bai wa jihohi damar su rinka samar da wutar lantarkinsu su ma.

Atiku ya kara da cewa, mafita ta biyu kuma bayan wannan ita ce kafin karin samun wutar lantarki sai an inganta hanyoyin rarrabata ta hanyar hadin gwiwar gwamnati da kuma kamfanoni masu zaman kansu.

Ya ce, hakan kuma zai yi wu ne idan aka kyale gwamnatin tarayya ta mayar da hankali kan tsare-tsare da sanya ido da kuma inganta hanyoyin samar da wutar lantarkin.

Atiku ya ce, yanayin da ya ga samar da lantarki a kasar na fuskantar matsaloli a cikin sa’oi 24 da aka yi babu wutar ya sa ya fara tunanin hanyoyin da zai bi wajen samar da maslaha a wannan bangare.

Ya ce, wannan tsari nasa na kunshe a cikin wani kundin da ya tsara kan yadda zai warware matsalolin da ake fuskanta a Najeriya.

fg spw news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp