fidelitybank

Zamu yi zanga-zanga tsirara a ofishin EFCC idan ba a gaggauta sakin tsohon gwamna Obiano – Ƙungiyar mata

Date:

Wasu ƙungiyar Mata a Anambra karkashin inuwar Anambra-North Women Empowerment Movement (AWEM), sun nuna rashin jin dadinsu kan ci gaba da tsare tsohon gwamnan jihar Anambra, Willie Obiano, inda suka sha alwashin yin zanga-zanga tsirara idan hukumar yaki da cin hanci da rashawa (EFCC) ta ci gaba da tsare shi a gidan yari ba tare da an gurfanar da shi a gaban kotun shari’a ba.

AWEM sun bayyana haka ne a lokacin da suke mayar da martani ga faifan bidiyo na Obiano a ofishin EFCC, inda aka ga tsohon gwamnan sanye da guntun wando da riga.

A cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Litinin, shugabar kungiyar ta AWEM, Uju Ifunanya Edochie yayin da ta ke nuna rashin jin dadin ta game da ci gaba da tsare Obiano, ta yi Allah wadai da kakkausar murya da abin da ta bayyana a matsayin rikon sakainar kashi da rashin da’a wajen gudanar da shari’ar.

Ta ci gaba da cewa hukumar EFCC ba ta da tsaro idan aka yi la’akari da yadda za a iya yin faifan bidiyon wani tsohon gwamna, inda ya kamata a ce yana tsare a hannun jami’an tsaro da aikewa da jama’a a shafukan sada zumunta, domin yi wa tsohon gwamnan ba’a.

Daga nan sai kungiyar ta yi barazanar cewa za ta yi zanga-zanga tsirara a ofishin EFCC na Abuja idan EFCC ba ta gaggauta sakin tsohon gwamna Obiano ba ko kuma ta kai shi kotu.

legit news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp