fidelitybank

Zamu yi zanga-zanga tsirara a ofishin EFCC idan ba a gaggauta sakin tsohon gwamna Obiano – Ƙungiyar mata

Date:

Wasu ƙungiyar Mata a Anambra karkashin inuwar Anambra-North Women Empowerment Movement (AWEM), sun nuna rashin jin dadinsu kan ci gaba da tsare tsohon gwamnan jihar Anambra, Willie Obiano, inda suka sha alwashin yin zanga-zanga tsirara idan hukumar yaki da cin hanci da rashawa (EFCC) ta ci gaba da tsare shi a gidan yari ba tare da an gurfanar da shi a gaban kotun shari’a ba.

AWEM sun bayyana haka ne a lokacin da suke mayar da martani ga faifan bidiyo na Obiano a ofishin EFCC, inda aka ga tsohon gwamnan sanye da guntun wando da riga.

A cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Litinin, shugabar kungiyar ta AWEM, Uju Ifunanya Edochie yayin da ta ke nuna rashin jin dadin ta game da ci gaba da tsare Obiano, ta yi Allah wadai da kakkausar murya da abin da ta bayyana a matsayin rikon sakainar kashi da rashin da’a wajen gudanar da shari’ar.

Ta ci gaba da cewa hukumar EFCC ba ta da tsaro idan aka yi la’akari da yadda za a iya yin faifan bidiyon wani tsohon gwamna, inda ya kamata a ce yana tsare a hannun jami’an tsaro da aikewa da jama’a a shafukan sada zumunta, domin yi wa tsohon gwamnan ba’a.

Daga nan sai kungiyar ta yi barazanar cewa za ta yi zanga-zanga tsirara a ofishin EFCC na Abuja idan EFCC ba ta gaggauta sakin tsohon gwamna Obiano ba ko kuma ta kai shi kotu.

www nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp