fidelitybank

Zamu yi garkuwa da Buhari da El-Rufa’i – ‘Yan ta’adda

Date:

‘Yan makwanni kadan bayan harin da aka kaiwa ayarin motocin shugaban kasa, Muhammadu Buhari a Dutsinma, jihar Katsina, yanzu ‘yan ta’adda sun yi barazanar sace shi nan na daya.

A wani sabon faifan bidiyo da ‘yan jarida suka fitar, ‘yan ta’addan da suka yi garkuwa da fasinjojin jirgin kasa sama da 60, sun yi barazanar yin garkuwa da su da kuma kashe shugaba Buhari da gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-rufai.

‘Yan ta’addan sun kuma yi alfahari da cewa, za su ruguza Najeriya tare da kashe sauran wadanda aka kashe a hannunsu. A cewar Politics Najeriya.

“Wannan shi ne sakonmu ga gwamnatin Najeriya kuma kamar yadda kuka ga wadannan mutane a nan, da yardar Allah za ku ga shugabanninku; Sanatoci da gwamnoninku za su zo gabanmu.”

“Wadannan da kuke gani a nan za mu ajiye wasu a matsayin bayi mu sayar da su kamar yadda Imaminmu ya fada muku a baya,” inji shi.

“Kamar yadda ’yan matan Chibok da aka sayar, za mu sayar da wadannan a matsayin bayi. Idan ba ku bi bukatunmu ba, za mu kashe wadanda muke bukata mu kashe mu sayar da sauran.”

“Da yardar Allah, El-Rufai da Buhari, za mu kawu ku nan.”

nigeria daily post

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp