Jam’iyyar APC ta ce za ta yanke shawara kan jadawalin zabukanta na fitar da gwani a ranar Laraba.
Za ta dauki matakin ne a yayin taron majalisar zartarwarta, wanda shugabannin jam`iyyar suka ce, zai mai da hankali ne wajen tattaunawa a kan shirin jam`iyyar na gudanar da zaben fid da gwani, domin tunkarar babban zaben 2023.
Wannan shi ne karon farko da kwamitin zartarwar APC zai yi zama bayan babban taron jam`iyyar, inda aka zabi sabbin shugabanni na kasa.
Kazalika taron ya zo ne a lokacin da hukumar zabe ta bai wa jam`iyyun siyasa wa`adin nan da watan Yuni mai zuwa su mika mata sunayen wadanda za su yi takara da tutocinsu