Dan takarar shugaban kasa a Najeriya na jam’iyyar Labour Party (LP), Mr Peter Obi, ya ce, zai tattauna da ‘yan haramtacciyar kungiyar nan ta masu fafutukar neman ‘yancin Biafra (IPOB) da sauran masu fafutuka domin maido da zaman lafiya kasar, idan aka zabe shi.
Mr Obi ya bayyana hakan ne a hira ta musamman da kafofin gidan jaridar Daily Trust, a Abuja yayin da yake amsa tambaya a kan matsalar tsaro a Najeriya.
Dan takarar na jam’iyyar Labour wanda tsohon gwamnan Jihar Anambra ne, ya ce salonsa zai zama daban da na takwarorinsa kan wannan matsala idan har aka zabe shi a ranar 25 ga watan Fabrairu na shekara mai kamawa 2023.
Obi ya ce, ya sha nanatawa ba sau daya ba ba sau biyu ba, cewa Najeriya ba ta da masu fafutuka fiye da kasar Brazil.
”Idan kana so zan nuna maka kasashen da suka yi fama da masu fafutuk a baya, ko Brazil ce ko Mexico ce, ko wannan ce.
”A kudu maso gabashinmu abu ne mai sauki, zan yi tattauna, zan tattauna, dumukuradiyya ce kuma a mulkin dumukuradiyya kana mulki ne da cimma matsaya. Idan wani ya ce ba ya jin dadi, sai ka kira shi ka zauna da shi ka tattauna da shi,” in ji Mista Obi.