fidelitybank

Zamu taka rawar gani a gasar kofin duniya ta mata – Alvine

Date:

Kyaftin din Flamingos, Alvine Dah-Zossu, ta gamsu da cewa kungiyar za ta nuna girmamawa a gasar cin kofin duniya ta mata na FIFA U-17 na 2022 a Indiya.

A halin yanzu ‘yan matan Bankole Olowookere suna Koceli, Turkiyya, don yin atisayen kwana 10 kafin gasar.

Kungiyar Flamingos ta lallasa Galatasaray Ladies da ci 3-1 a wasan sada zumunta da suka yi a ranar Asabar da ta gabata.

‘Yan matan Najeriya za su kara da Fenerbahce Ladies a wani wasan sada zumunta nan gaba a cikin wannan mako.

Yayin da suke ci gaba da shirye-shiryensu na gasar, Dah-Zossu ta jadada shirin kungiyar na taka rawar gani a Indiya.

“Kowace ranar horo wata dama ce ta koyo, abubuwa masu kyau ba su zo cikin sauƙi amma mun kuduri aniyar yin kyau a gasar cin kofin duniya na mata na 17 na FIFA. Ba za mu huta ba har sai mun cimma burinmu,” kamar yadda ta shaida wa thenff.com.

A ranar Talata 11 ga watan Oktoba ne kungiyar Flamingos za ta kara da Jamus a wasansu na farko a gasar a Goa.

nnn.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnan Kano ya kori mataimansa na musamman kan belin Danwawu

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da...

Tsohon Minista a mulkin Buhari ya mutu

Allah ya yi wa tsohon ministan noma da raya...

Kashi 70 na yankin Bukuyum ta Kudu na ƙarƙashin ƴan Bindiga – Ɗan majalisa

Rahotanni daga yakin ƙaramar hukummar Bukuyum na jihar Zamfara...

Goodluck ya fi dacewa ya zama dan takara a 2027 – Lamido

Tsohon Gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido ya ce Tsohon...

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...
X whatsapp