fidelitybank

Zamu taimakawa Najeriya wajen gano wanda suka kashe ma’aikatan mu – Amurka

Date:

Gwamnatin Amurka ta yi alkawarin taimakawa Najeriya, wajen cafke wadanda suka kashe jami’anta da ‘yan sanda biyu a Anambra.

Wasu gungun wasu da ba a san ko su waye ba a ranar Talata sun kai hari kan ayarin motocin gwamnatin Amurka biyu a karamar hukumar Ogbaru.

ayarin motocin na dauke da ‘yan Najeriya 9 da ma’aikatan ofishin jakadancin Amurka biyar da kuma jami’an ‘yan sandan Najeriya hudu.

Tawagar ta yi tattaki ne gabanin wata ziyarar da ta shirya kai wa wani aikin shawo kan ambaliyar ruwa a Anambra wanda gwamnatin Amurka ta dauki nauyi.

A wata sanarwa da ofishin jakadancin ya fitar a daren Laraba ta ruwaito sakataren harkokin wajen Amurka, Antony Blinken yana cewa har yanzu Amurka ba ta san dalilin kai harin ba da kuma ko an kai harin ne kan Ofishin Jakadancin.

“Maharani sun kashe akalla mutane hudu daga cikin ayarin motocin. Hukumomin Amurka na hada kai da takwarorinsu na Najeriya domin sanin wurin da wadanda lamarin ya shafa ba a san inda suke ba.

“Muna yin Allah wadai da wannan harin. Za mu yi aiki kafada da kafada da takwarorinmu na jami’an tsaron Najeriya wajen neman gurfanar da wadanda ke da hannu a gaban kuliya, “in ji Blinken.

Amurka ta ce ba ta da fifiko fiye da tsaro da tsaron jami’anta, tana mai jajantawa iyalan wadanda aka kashe a harin.

Sanarwar ta kuma kara jaddada aniyar Amurka ga al’ummar Najeriya na taimakawa wajen yaki da tashe-tashen hankula da rashin tsaro.

nigeria news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp