fidelitybank

Zamu tabbatar ba sunayen bogi a masu zabe – Jam’iyyu

Date:

Jam’iyyu na ci gaba da bayyana ra’ayoyinsu, tun bayan gabatar musu da kundin rijistar masu zaɓe da Hukumar zabe ta kasar, INEC ta yi a ranar Laraba.

Cikin adadin masu zaɓe sama da miliyan 93 da kundin rijistar ya ƙunsa, maza ne suka fi yawa inda suka kai sama da miliyan 49, sai mata su kuma sama da miliyan 44.

Injiniya Yabagi Sani shi ne shugaban kwamitin tuntuɓa tsakanin jam’iyyu wato IPAC.

Ya ce dokar zabe ta kasa ta tilastawa hukumar zaben ta mika wa dukkan jam’iyyun siyasa na kasar kundin rajistar masu zaben da ta hada.

“Wannan zai ba jam’iyyu damar sanin inda wadanda aka yi wa rajista suke, da inda za a same su. Kan haka ne jam’iyyun za su iya sanin adadin wadanda suka yi rajistar da inda za iya samunsu.”

Ya ce bayan sun karbi rajistar zaben, jam’iyyun siyasar za su gudanar da bincike kan wadanda ke da katin zabe wato PVC da ‘yan jam’iyyar da ba su da katin samsam. In ji BBC.

Kan ko jam’iyyun siyasar sun gamsu da kundin masu rajistar, Injinaya Yabagi ya ce a baya akwai damuwa cewa rajistar zaben ta kunshi sunayen wasu mutane na bogi, amma bayan an gudanar da bincike mai zurfi, an gano ba haka lamarin yake ba.

“Wannan duka babu kurakurai yanzu. In dai Allah yasa INEC ta yi aiki da wannan rajistar kamar yadda aka tsara, da kuma yadda suka yi alakawarin yi, to ina ganin zai kawo wani sauyi mai ma’ana.”

Ya yi kira ga hukumar zaben da ma jam’iyyun siyasa na Najeriya, da su tashi tsaye wajen wayar da kawunan al’ummar kasar.

“Ya kamata mu sami jama’a domin mu tabbatar sun karbi katunan zabensu daga hukumar zabe, domin wannan zai ba mu damar tabbatar da sunayen da aka wallafa a kundin zaben masu sahihanci ne, ba cushe aka yi ba.”

the nation newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iya wa’adi daya ya ishe ni a mulkin Najeriya – Peter Obi

Tsohon ɗan takarar shugabancin Najeriya a jam'iyyar Labour, Peter...

Luis Diaz ya zaba wa kansa makoma da ya bar Liverpool – James

Kyaftin din Colombia, James Rodríguez, ya dage cewa dan...

Ka fito ka baiwa Matawalle hakuri ko ka fuskanci fushin kotu – Shinkafi

Wani mai fafutukar kare hakkin bil’adama, Dakta Suleiman Shuaibu...

Liverpool za su sayar da ‘yan wasa uku su dauki Isak

Liverpool a shirye take ta sayar da matasan yan...

Ba zamu daga wa Hamas kafa ba har sai an saki mutanen mu – Netanyahu

Firaiministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, ya yi dogon...

Za mu gyara tsarin Maiduguri saboda ambaliya – Zulum

Gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum ya ce, gwamnatinsa...

Dubban mutane sun yi zanga-zangar goyon bayan Falasɗinawa a Australia

Dubban mutane ne suka gudanar da zanga-zangar goyon bayan...

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...

Facebook ya ƙi amincewa da tsare-tsaren Turai na amfani da AI

Wasu muhimman tsare-tsare na dokokin Tarayyar Turai kan amfani...

Ranar 18 za a fara rajistar zabe – INEC

Hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC ta sanar da...

Trump ya tura jiragen ruwa na yaki masu dauke da makaman nukiliya kusa da Rasha

Shugaba Trump ya ce, ya umarci a matsar da...

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da...
X whatsapp