fidelitybank

Zamu mayar da martanin ƙarfin tuwo idan ECOWAS ta taɓa mu – Nijar

Date:

Sabuwar gwamnatin sojin Nijar, ta ce za ta mayar da martani ba tare da bata lokaci ba ga duk wata takala ko yunkurin takala daga kasashen yammacin Afirka.

Gargadin ya zo ne kwana uku kafin karewar wa’adin da kungiyar Ecowas ta ba wa Nijar din na a dawo da kasar kan turbar tsarin mulki.

Sojojin sun ce sun soke wasu yarjejeniyoyin soji da aka kulla tsakanin Shugaba Bazoum da Faransa bayan sun karbe ikon kasar.

Jakadan Nijar a Amurka, Kiari Liman Tinguiri wanda sojojin suka kora, ya ce ”idan Nijar ta durkushe to baki dayan yankin Sahel abin ya shafa, sannan yankin zai fuskanci babbar matsala, idan kuwa har aka samu matsala a yankin to kare kasashen ma zai yi matukar wuya”.

Cikin mukalar da ya rubuta a jaridar Washington Post, Shugaba Bazoum ya ce an yi garkuwa da shi inda ya yi kira ga Amurka da ma sauran kasashen Yamma a kan su taimaka a dawo da kasar kan turbar tsarin mulki.

Ya kuma yi gargadin cewa muddin aka bari juyin mulkin kasar ya yi tasiri to hakan zai haifar da mummunan sakamako.

vanguard news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp