fidelitybank

Zamu kwace lasisin bankin da ya ki bayar da sababbin kudi – Zulum

Date:

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya gargaɗi bankunan kasuwanci a jihar cewa gwamnatinsa za ta ƙwace lasisin filin duk bankin da ya gaza saka sabbin takardun naira a na’urorin cire kuɗi na ATM.

Gwamnan ya yi gargaɗin ne ranar Juma’a a birnin Maiduguri lokacin da ya kai ziyara don gane wa idonsa irin dogwayen layuka da wahalar da jama’a ke fuskanta na ƙarancin sabbin takardun kuɗin.

“Duk bankin da ba shi da niyyar cika ATM ɗinsa da sababbin takardun kuɗi don sauƙaƙa wa al’umma wahalhalu, za mu ƙwace filin gininsa nan take,” in ji gwamnan cikin wata sanarwa da kakakinsa Isa Gusau ya fitar.

Karanta Wannan: Mun karbi Naira biliyan 18.6 na gyaran titi a hannun gwamnatin tarayya – Kuros Riba

Sanarwar ta ce ran Gwamna Zulum ya ɓaci ne lokacin da ya tarar da wani dogon layin cirar kuɗi, inda ATM ɗaya ne kacal yake aiki cikin 10 da ke wurin.

“Kamar yadda kuke gani, talakawa ne kawai a kan layi…An ce wasu tun ƙarfe 3:00 na dare suke a nan, wasu ma ba su ci komai ba. Sababbin kuɗin da tsofaffin duka babu, wanda hakan ke shafar harkokin kasuwanci tare da ƙuntata wa mutane,” a cewar Zulum.

Gwamnan ya ƙara da cewa lokacin da ya je Ƙaramar Hukumar Gubio ya tarar cewa babu naira N100,000 a faɗin ƙaramar hukumar baki ɗaya na tsofaffi ko sababbin kuɗin.

legit latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaɗi masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga Falasɗinawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Lauyoyin ffitaccen ɗan gwagwarmayar nan kuma ɗan jarida, Omoyele...

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...
X whatsapp