Wani jigon al’ummar masarauta kuma tsohon Manajan Daraktan Hukumar Yada Labarai ta Jihar Kaduna (KSMC), Alhaji Zubairu Idris Abdulra’uf, ya yi na’am da wannan umarni na ‘yan bindiga a Masarautar Birnin-Gwari ta Jihar Kaduna, da kalaman gwamnan Zamfara ya yi na cewa, kamata mutane su yi kokarin kare kansu, yana mai bayyana cewa, tuni mutanen masarautunsa suka amince da wannan zabin.
Abdulrra’uf ya bayyana haka ne a wata hira da ya yi da cewa, hare-haren da ake kai wa jama’ar sa gaba daya ya durkusar da harkokin tattalin arziki a yankunansu na karkara, ya kuma sanya tafiye-tafiye a yankunan ke da wahala ko ma ba zai yiwu ba a wasu wuraren.
A cewarsa, “mun kai ga rashin dawowa. Ana tura mutane bango. Jiya Randegi na daya daga cikin wuraren da wadannan ‘yan fashin ke bi ta jihar Zamfara zuwa jihar Neja.”
“Mutanen Randegi sun fuskanci wadannan ‘yan bindiga da suka yi kokarin mamaye garin Randegi, wata al’ummar manoma, kuma sun yi nasarar fatattakar wadannan ‘yan bindigar. Don haka ina ganin mutanenmu a shirye suke idan har gwamnati ba za ta iya gudanar da ayyukanta na tsarin mulki ba.”
Tsohon mai watsa labarai na gidan rediyon DW ya ce, sama da shekaru 2 ‘yan bindigar sun sanya haraji kan manoman Birni-Gwari, yana mai jaddada cewa.
“Eh, an biya Naira miliyan 200 ga ‘yan bindiga a gundumar Randegi kadai.”