fidelitybank

Zamu kai sojojin mu wata kasar bayan mun fice daga Nijar – Amurka

Date:

Kwamandan dakarun Amurka a Turai da Afirka ya ce sun fara shirin ɗaukar matakai idan aka nemi su fice daga Nijar ciki har da neman ƙasar da za su mayar da su a yammacin Afirka, kamar yadda kafofin labaran Amurka suka ruwaito.

“Za mu kasance cikin shiri idan wani abu ya faru,” a cewar Janar James Hecker yayin tattaunawarsa da manema labarai ta intanet a ranar Juma’a.

“Akwai matakai da za mu iya ɗauka da yawa idan za mu fice [daga Nijar]. Dole ne dai mu zama a shirye don ɗaukar dukkan matakan…amma muna fatan ba za ta kai ga haka ba.

“Dole za mu duba wasu ƙasashen da za mu yi ƙawance da su a [yammacin] Afirka da za mu mayar da kayan aikinmu can.”

Amurka na da dakaru aƙalla 1,000 a Nijar da ke aikin yaƙi da masu iƙirarin jihadi a yankin Sahel, kuma har yanzu ba ta ayyana kifar da gwamnatin Bazoum a matsayin juyin mulki ba.

Da zarar Amurka ta ayyana lamarin a matsayin juyin mulki, hakan zai shafi alaƙarta da Nijar kai-tsaye, abin da ka iya kawo ƙarshen tallafin da take bai wa ƙasar da kuma zaman dakarun nata a can.

sun news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp