fidelitybank

Zamu jaddada sahihin zabe da cikakkiyar demokradiya – Buhari

Date:

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bayyana kudurinsa na kara zurfafa dimokaradiyya a kasar nan tare da kafa misali mai kyau ga sauran kasashen Afirka ta hanyar tabbatar da sahihin zabe a 2023.

Buhari ya bayyana haka ne a ranar Litinin a Abuja, a wajen bukin ranar ‘yan kasashen waje na Najeriya karo na 16 na shekarar 2022, kuma karo na 4 da hukumar ‘yan Najeriya mazauna kasashen waje (NiDCOM) za ta shirya.

Ranar, wadda ake bikin ranar 25 ga watan Yuli, kowace shekara, tana da taken: Hidimar Al’umma a Zamani masu Kalubalantar Duniya don Ci gaban Kasa.
Shugaban wanda ya samu wakilcin shugaban ma’aikatan sa, Farfesa Ibrahim Gambari, ya ce nasarar dimokuradiyyar Najeriya za ta hana hanyoyin samun sauyin gwamnati da bai dace ba a yankin da sauran sassan nahiyar Afirka.

A cikin shekara guda ne nahiyar Afirka ta shaida yadda sojoji suka mamaye kasashen Chadi, Mali, Guinea Bissa, Burkina Faso da Sudan.

Buhari ya ce: “Kamar yadda kuka sani cewa shirye-shiryen zabukan kasarmu na 2023 sun ci gaba da tafiya cikin kwanciyar hankali kuma sun yi daidai da dokokin kasarmu da tsarin mulkinmu.

“Na sha ba da tabbacin kuduri na na kashin kaina, da na gwamnatina na tabbatar da cewa al’amura sun ci gaba da kasancewa a bayyane, a yi sahihanci, da tabbatar da gaskiya da adalci, wanda zai kai ga gudanar da zabe cikin lumana, da mika mulki ga gwamnati mai zuwa. .

punch newspaper headlines today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp