‘Yan sanda a jihar Gombe, sun kama wasu mutane da ake zargi sun shigo Najeriya ba bisa ka’ida ba.
Mutanen wadanda ake zargi sun shigo daga jamhuriyar Benin su hudu da kuma wasu biyu ‘yan Najriya.
Akalla mutane 109 ne ke kwantar da hankula a rundunar ‘yan sandan jihar Gombe bisa zargin shigowa da kasar ba bisa ka’ida ba daga jamhuriyar Benin.
Da yake bayyana hakan a wani taron manema labarai, kwamishinan ‘yan sanda jihar, Ishola Babaita, ya ce an shigo da mutanen ne ta cikin wasu motocin bas guda uku daga kasar Benin, tare da goyon bayan ‘yan Najeriya masu hadin gwiwa.
Babaita ya ce, da aka yi musu tambayoyi, wadanda ake zargin sun yi ikirarin cewa su mambobi ne na QNET, wani tsarin sadarwar na internet.
Ya ce, “A ranar 18 ga watan Janairun 2022, rundunar ta samu labarin cewa, motocin bas guda uku ne suka kawo wasu gungun samari 109.
Yayin da ya bukaci jama’a da su yi taka-tsan-tsan wajen yin sana’ar ta haramtacciyar hanya, domin kuwa ya ce, za a gurfanar da duk wadanda ake zargin a gaban kuliya.