fidelitybank

Zamu fara faɗan sakamakon zaɓe da tsakar ranar yau – INEC

Date:

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), ta ce, za ta fara tattara sakamakon zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisar dokoki na shekarar 2023 a ranar Lahadi da tsakar rana.

Shugaban hukumar ta INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya sanar da hakan, a wani taron manema labarai kan zaben 2023 da aka yi ranar Asabar a Abuja.

Yakubu ya ce, hukumar na sa ran samun sakamako daga jihohin daga ranar Lahadi.

“Zan so in gayyace ku da tsakar rana a gobe Lahadi, domin bude cibiyar tattara sakamakon ta kasa a hukumance.

“Muna fatan zuwa gobe, muna sa ran samun wasu sakamakon zaben da za su fito daga jihohi, musamman na zaben shugaban kasa.

“Don haka, cibiyar tattara sakamakon zaben shugaban kasa za ta bude da tsakar rana,” in ji Yakubu.

Ya kara da cewa ba za a bukaci a yi wa ‘yan Najeriya jawabi ba kafin ranar Lahadi (26 ga Fabrairu), sai dai idan akwai bukatar yin hakan.

nasarawa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp