fidelitybank

Zamu dawo da zaman lafiya Ukraine – Zelensky

Date:

Shugaban kasar Ukraine, Volodymyr Zelensky ya ce, ya tattauna da shugaban kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan, kuma bangarorin biyu sun amince da bukatar farfado da zaman lafiya a kasarsa a yayin yakin da ake yi tsakanin Ukraine da Rasha.

Baki daya, mun amince da bukatar dawo da zaman lafiya. Mun yaba da taimakon Turkiyya a wannan tsari, ”Zelensky ya wallafa a shafinsa na Twitter a daren Litinin bayan tattaunawar.

A yayin tattaunawar, Zelensky da Erdogan sun kuma tattauna kan barazanar samar da abinci sakamakon rikicin Rasha da Ukraine da kuma hanyoyin da za a bi wajen toshe tashoshin jiragen ruwa na Ukraine.

Sun kuma tattauna hadin gwiwa a fannin tsaro.

Sanarwar da ofishin Erdogan ya fitar ta ce, Turkiyya na ba da muhimmanci ga aikin samar da amintacciyar hanya don fitar da kayayyakin amfanin gona na Ukraine ta ruwa.

Sanarwar ta ce, Turkiyya ta yi iyakacin kokarinta na ci gaba da tattaunawa tsakanin Ukraine da Rasha.

Har ila yau, ta ce a shirye Turkiyya ta ke ta ba da tallafin da ake bukata, ciki har da shiga tsakani.

Tun da farko, Erdogan ya tattauna ta wayar tarho da shugaban Rasha, Vladimir Putin.

sspdf news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp