fidelitybank

Zamu dawo da zaman lafiya Ukraine – Zelensky

Date:

Shugaban kasar Ukraine, Volodymyr Zelensky ya ce, ya tattauna da shugaban kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan, kuma bangarorin biyu sun amince da bukatar farfado da zaman lafiya a kasarsa a yayin yakin da ake yi tsakanin Ukraine da Rasha.

Baki daya, mun amince da bukatar dawo da zaman lafiya. Mun yaba da taimakon Turkiyya a wannan tsari, ”Zelensky ya wallafa a shafinsa na Twitter a daren Litinin bayan tattaunawar.

A yayin tattaunawar, Zelensky da Erdogan sun kuma tattauna kan barazanar samar da abinci sakamakon rikicin Rasha da Ukraine da kuma hanyoyin da za a bi wajen toshe tashoshin jiragen ruwa na Ukraine.

Sun kuma tattauna hadin gwiwa a fannin tsaro.

Sanarwar da ofishin Erdogan ya fitar ta ce, Turkiyya na ba da muhimmanci ga aikin samar da amintacciyar hanya don fitar da kayayyakin amfanin gona na Ukraine ta ruwa.

Sanarwar ta ce, Turkiyya ta yi iyakacin kokarinta na ci gaba da tattaunawa tsakanin Ukraine da Rasha.

Har ila yau, ta ce a shirye Turkiyya ta ke ta ba da tallafin da ake bukata, ciki har da shiga tsakani.

Tun da farko, Erdogan ya tattauna ta wayar tarho da shugaban Rasha, Vladimir Putin.

the sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Wa’adin da Najeriya ta bai wa Facebook na biyan tarar dala miliyan 290 ya cika

A ranar Litinin ne wa'adin da wata kotu ta...

Jami’an sa-kan Zamfara sun kashe Kacalla Ɗanbokolo ubangidan Turji

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammcin Najeriya...

PDP ta gudanar da taron ta na kasa

Shugabani da gwamnonin da sauran masu ruwa da tsaki...

An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa Talata

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...

Tawagar Gwamnatin Kano ta shilla Saudiyya zuwa jana’izar Dantata

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci...

Tawagar Jami’an gwamnati da Malamai sun tafi jana’izar Dantata

Wata tawaga daga gwamnatin Tarayya, ta isa ƙasar Saudiyya...

Taimakon da Dantata ya ke yi wa Al’umma tarihi ba zai manta da shi ba – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa...

Gwamnan Kano ya sauya wa hukumar Wasanni suna

Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya sauya wa...

Dalilin da ya sa Wake ya karye a Najeriya – Ƙungiyar Manoma

Ƙungiyar manoman wake a kasar nan, ta bayyana amfani...

Masu shan Taba Sigari sun shiga rudani a Faransa da firgici

A yau ne sabbin dokokin hana shan taba a...
X whatsapp