Shugaba kasa Muhammadu Buhari, ya kaddamar da shirin samar da hanyoyin bada tazarar haihuwa na zamani a Najeriya.
Buhari ya ce an kaddamar da shirin ne, domin inganta rayuwar ‘yan Najeriya, wanda hakan na cikin ababen da gwamnatin ke son cimma a kai.
Tuni dai an kafa wani kwamiti na musamman da zai saka ido kan yawan al’umma a Najeriya da Shugaba Buhari da kansa zai shugabanta.
Shugaba Muhammadu Buhari ya bukaci a dauki matakan gaggawa game da yawan haihuwa da ake yi a Najeriya ta hanyar fadada shirin samar da hanyoyin bada tazarar haihuwa a sassan kasar nan. A cewar Tribune.