Shugaban Hukumar Kula da kidaya ta Kasa (NPC), Nasir Isa Kwarra, ya bayyana cewa, hukumar za ta dauki nauyin ma’aikatan wucin gadi miliyan 1.5 a yayin kidayar gidaje da yawan jama’a mai zuwa da za a yi a watan Afrilun 2023.
Kwarra wanda ya bayyana hakan a ranar Asabar a wani shirin rediyo kai tsaye wanda Sunday Independent ke sa ido, ya ce za a fitar da sakamakon kidaya ta hanyar lambobi ga masu ruwa da tsaki da cibiyoyin samar da bayanai don tsare-tsare da bincike na kasa.
Ya bayyana cewa tsari da kuma gudanar da kidayar za ta zama na dijital, don tabbatar da daidaiton aikin kidayar.
Don haka, ya bukaci ’yan Najeriya da suka cancanta da su ziyarci tashar kuma su yi amfani da shafin Internet na Hukumar.
Jalingo ya nemi goyon baya da hadin kan ‘yan Najeriya, don ganin an samu nasarar kidayar jama’a.