fidelitybank

Zamu binciki ta yadda ƴan siyasa ke siyan tikitin takara – EFCC

Date:

Shugaban Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati, EFCC, Abdulrasheed Bawa, a karshe ya bayyana cewa, hukumar na sa ido sosai kan masu neman tsayawa takara a zaben 2023.

POLITICS NIGERIA ta tuna cewa, an yi ta cece-kuce daga ‘yan Najeriya bayan da jam’iyyar APC mai mulki ta tsayar da farashin tikitin kuɗin takararta na shugaban kasa a 2023 a kan Naira miliyan 100.

Jama’a da dama dai sun yi kira ga hukumar yaki da cin hanci da rashawa da ta gaggauta binciken duk wani mai neman tsayawa takara da ya biya kudin fam dinsa. Da yake mayar da martani kan wannan ci gaba a wata hira da gidan talabijin na Channels TV, Bawa ya ce;

“Idan aka zo batun sa ido kan kudaden zabe da kuma kudaden ‘yan takara, wannan yana da alaka da aikin INEC a wannan fanni amma, ba shakka muna aiki kafada da kafada da INEC da sauran hukumomin da ke da alaka a wannan fanni. don tabbatar da cewa mun bi kudin, mun san madogaran, shin halas ne ko kuma na haram ne, domin abin da ya shafe mu ke nan.”

Ya zuwa yanzu dai Bola Ahmed Tinubu da Fasto Tunde Bakara da Yemi Osinbajo da Godwin Emefiele da Ken Nnamani da Rotimi Amaechi da Ogbonnaya Onu da Emeka Nwajiuba da Ibikunle Amosun da Rochas Okorocha sun karbi fom din takarar shugaban kasa na Naira miliyan 100.

legit com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp