fidelitybank

Zamfara: ‘Yan ta’adda sun kona mutane a mota tare da yin garkuwa da wasu

Date:

Rahotanni na nuni da cewa, akalla mutune shida a ka kashe, yayin da a ka yi garkuwa da wasu mutane da dama, bayan da ‘Yan tadda suka tare hanyar Kauran Namoda zuwa Shinkafi a Jihar Zamfara.

Mazauna yankin sun shaida wa wakilin Aminiya cewa maharan sun kuma banka wa wasu daga cikin motocin da su ka tare wuta da fasinjoji a ciki, kuma ko gawarwakinsu ba a iya ganewa.

A cewarsu, akasarin maharan, wadanda yaran kasurgumin dan bindigar nan ne da aka fi sani da Turji, sun zafafa kai hare-hare a yankin a cikin ’yan kwanakin nan, tun bayan da wani harin sojojin sama ya kashe masa wata gwaggo da mijinta da kuma mayakansa da dama.

’Yan bindigar sun tare hanyar ce a daidai tsakanin Kwanar Jangeru da Moriki, wacce dama tuni matafiya su ka daina bi, saboda rashin tsaro. Babu wanda zai iya zuwa ma ya kwaso gawarwakin mutanen da a ka kashe”. inji wani mazaunin yankin da ya nemi a sakaya sunansa.

Shi kuwa wani mazaunin yankin mai suna Mansur cewa ya yi, “Ka san harin da sojojin sama suka kai kwanan nan ne ya fusata su. Harin ya ragargaza daya daga cikin sansanonin Turji, sannan ya kashe ’yan uwansa da yaransa da dama”.

Sai dai wasu majiyoyin sun ce ’yan bindigar sun dawo da kai hare-haren ne, domIn su nuna bacin ransu da ci gaba da rufe kasuwar dabbobi ta garin Shinkafi.

An dai jiyo wasu daga cikinsu na cewa za su ci gaba da kai hare-hare a yankin har sai lokacin da aka sake bude kasuwar dabbobin.

Aminiyar ta kuma tuntubi mai magana d’yan sandan Jihar, SP Muhammad Shehu, ya ce, a ba shi lokaci zai tuntuba daga bisani, ko da ya ke bai yi hakan ba har zuwa lokacin hada wannan rahoton.

 

 

 

 

 

latest legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa a Najeriya ta ce...

Shugaban Laberiya ya je ta’aziyyar Buhari a Monrovia

Shugaban Ƙsaar Laberiya Joseph Nyuma Boakai ya kai ziyarar...

Rundunar Yansandan Kaduna ta hana gangamin goyon bayan Peter Obi

Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta hana gudanar...

Iran ta zartar da hukuncin kisa a kan Mutane 3

Hukumomi a Iran sun zartar wa mutum uku hukuncin...

Ƴansanda sun kama ƙasurgumin ɗanbindiga a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna ta ce, jami'an ta sun...

Sudan ta Kudu ta yi ta’aziyyar Buhari

Mukaddashin Ministan Harkokin Wajen Sudan ta Kudu, Ambasada Akuei...

Trump ya na fama da cuta mai kumbura kafa da toshewar hanyar jini

A ranar Alhamis ne Fadar White House ta sanar...

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...
X whatsapp