fidelitybank

Zamfara: ‘Yan ta’adda sun kona mutane a mota tare da yin garkuwa da wasu

Date:

Rahotanni na nuni da cewa, akalla mutune shida a ka kashe, yayin da a ka yi garkuwa da wasu mutane da dama, bayan da ‘Yan tadda suka tare hanyar Kauran Namoda zuwa Shinkafi a Jihar Zamfara.

Mazauna yankin sun shaida wa wakilin Aminiya cewa maharan sun kuma banka wa wasu daga cikin motocin da su ka tare wuta da fasinjoji a ciki, kuma ko gawarwakinsu ba a iya ganewa.

A cewarsu, akasarin maharan, wadanda yaran kasurgumin dan bindigar nan ne da aka fi sani da Turji, sun zafafa kai hare-hare a yankin a cikin ’yan kwanakin nan, tun bayan da wani harin sojojin sama ya kashe masa wata gwaggo da mijinta da kuma mayakansa da dama.

’Yan bindigar sun tare hanyar ce a daidai tsakanin Kwanar Jangeru da Moriki, wacce dama tuni matafiya su ka daina bi, saboda rashin tsaro. Babu wanda zai iya zuwa ma ya kwaso gawarwakin mutanen da a ka kashe”. inji wani mazaunin yankin da ya nemi a sakaya sunansa.

Shi kuwa wani mazaunin yankin mai suna Mansur cewa ya yi, “Ka san harin da sojojin sama suka kai kwanan nan ne ya fusata su. Harin ya ragargaza daya daga cikin sansanonin Turji, sannan ya kashe ’yan uwansa da yaransa da dama”.

Sai dai wasu majiyoyin sun ce ’yan bindigar sun dawo da kai hare-haren ne, domIn su nuna bacin ransu da ci gaba da rufe kasuwar dabbobi ta garin Shinkafi.

An dai jiyo wasu daga cikinsu na cewa za su ci gaba da kai hare-hare a yankin har sai lokacin da aka sake bude kasuwar dabbobin.

Aminiyar ta kuma tuntubi mai magana d’yan sandan Jihar, SP Muhammad Shehu, ya ce, a ba shi lokaci zai tuntuba daga bisani, ko da ya ke bai yi hakan ba har zuwa lokacin hada wannan rahoton.

 

 

 

 

 

sunnnewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp