Rahotanni na nuni da cewa, akalla mutune shida a ka kashe, yayin da a ka yi garkuwa da wasu mutane da dama, bayan da ‘Yan tadda suka tare hanyar Kauran Namoda zuwa Shinkafi a Jihar Zamfara.
Mazauna yankin sun shaida wa wakilin Aminiya cewa maharan sun kuma banka wa wasu daga cikin motocin da su ka tare wuta da fasinjoji a ciki, kuma ko gawarwakinsu ba a iya ganewa.
A cewarsu, akasarin maharan, wadanda yaran kasurgumin dan bindigar nan ne da aka fi sani da Turji, sun zafafa kai hare-hare a yankin a cikin ’yan kwanakin nan, tun bayan da wani harin sojojin sama ya kashe masa wata gwaggo da mijinta da kuma mayakansa da dama.
’Yan bindigar sun tare hanyar ce a daidai tsakanin Kwanar Jangeru da Moriki, wacce dama tuni matafiya su ka daina bi, saboda rashin tsaro. Babu wanda zai iya zuwa ma ya kwaso gawarwakin mutanen da a ka kashe”. inji wani mazaunin yankin da ya nemi a sakaya sunansa.
Shi kuwa wani mazaunin yankin mai suna Mansur cewa ya yi, “Ka san harin da sojojin sama suka kai kwanan nan ne ya fusata su. Harin ya ragargaza daya daga cikin sansanonin Turji, sannan ya kashe ’yan uwansa da yaransa da dama”.
Sai dai wasu majiyoyin sun ce ’yan bindigar sun dawo da kai hare-haren ne, domIn su nuna bacin ransu da ci gaba da rufe kasuwar dabbobi ta garin Shinkafi.
An dai jiyo wasu daga cikinsu na cewa za su ci gaba da kai hare-hare a yankin har sai lokacin da aka sake bude kasuwar dabbobin.
Aminiyar ta kuma tuntubi mai magana d’yan sandan Jihar, SP Muhammad Shehu, ya ce, a ba shi lokaci zai tuntuba daga bisani, ko da ya ke bai yi hakan ba har zuwa lokacin hada wannan rahoton.