Kungiyar kwallon kafa ta Nigeria National League (NNL), Zamfara United ta nada Adamu Abdullahi a matsayin sabon kocinta.
A yau ne kuma ake sa ran kulob din zai gabatar da Abdullahi.
Matashin dan wasan ya taba bugawa Zamfara United wasa.
Zai yi niyyar jagorantar kungiyar zuwa gasar Premier ta Najeriya (NPFL).
Kungiyar kwallon kafa ta Zamfara United ta kasa samun nasarar zuwa gasar ta daya a kakar wasan data gabata.
An kori shugaban kungiyar Mohammed Alhassan a karshen kamfen din da ya gabata.