Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle, ya ba da tabbacin cewa, al’ummomin da tun farko ke fuskantar kalubalen tsaro a yanzu sun kasance cikin lumana da samun damar gudanar da zabukan 2023 mai zuwa.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a gidan sa dake karamar hukumar Maradun a lokacin da yake magana kan batun mafi karancin albashi na N30,000 ga ma’aikatan jihar, ‘yan daba da sauran batutuwa.
Gwamna Matawalle ya bukaci ‘yan Najeriya da su ci gaba da baiwa jami’an tsaro goyon baya, domin ganin an kawo karshen matsalar rashin tsaro da ke addabar kasar baki daya domin dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali.
Ya ce, bai san inda aka samu labarin cewa, za a dage zaben da ke tafe ba saboda rashin tsaro, ya na mai watsi da rade-radin da ake yi na cewa ‘yan Arewa za su goyi bayan dan takarar shugaban kasa na Arewa ne kawai.
Gwamnan ya bayyana cewa, gwamnatin sa ta aiwatar da mafi karancin albashi na N30,000 kuma an shirya samar da gidaje ga ma’aikata a wani bangare na kokarin inganta jin dadin su domin samun karin aiki.