Gwamnatin jihar Oyo karkashin jagorancin gwamna Seyi Makinde, za ta tattauna da kungiyoyin ‘yan daban cikin unguwa da na ‘yan asiri domin dawo da zaman lafiya a jihar.
Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa, waɗan nan ƙingiyoyin na ‘yan daba da ‘yan asiri, sune suka hana zaman lafiya a jihar Oyo ta hanyar kashe-kashen al’umma.
Kwamishinan yada labarai da wuraren bude ido, Dr. Wasiu Olatunbosun, shi ne ya bayyana shirin da gwamnati ta ke yi bayan ganawa da shugabannin jami’an tsaron wasu ƙungiyoyi.
Olatunbosun ya ce, gwamnatin jiha tare da haɗin kan kungiyoyin ‘yan Sa kai ta shirya warware matsalolin dake tsakanin ‘yan daban Anguya da yan asiri.
A cewar kwamishinan wannan zubar da jinin da yaƙi ci yaƙi cinye wa lokaci ya yi da za’a kawo ƙarshen shi a jihar Oyo.