Ministan yada labarai da al’adu, Lai Mohammed, ya bayyana cewa, bai taba jin ra’ayin yin watsi da jam’iyyar APC mai mulki ba.
Mohammed, a cikin wata sanarwa da ya sanya wa hannu, ya ce, barin jam’iyyar ba abu ne da zai taba yiwuwa ba.
Ya roki wadanda watakila su ka bar jam’iyyar su koma jam’iyyar.
Basu gamsu da yadda ake tafiyar da rikicin jihar Kwara ba, wasu magoya bayan Ministan suka fara ficewa daga jam’iyyar.
Sai dai a wata sanarwa da Ministan ya fitar ya yi kira gare su da su dawo, domin barin APC ba abu ne da zai taba yiwuwa ba.
Ya ce: “ Hankalina ya karkata ga yadda kafafen yada labarai suka rika yada labarin ficewar wasu magoya bayana na jam’iyyar APC a jihar Kwara zuwa jam’iyyar Social Democratic Party (SDP).