Wasu Zakuna biyu da ake kula da su a wani gidan ajiyar namun daji a kasar Iran, sun kashe mutumin da ya ke ba su abinci.
Shaidun gani a gidan namun dajin dake birnin Arak na kasar Iran sun ce, zakunan sun tsere daga kejin na su bayan sun kashe mutumin.
Jami’ai sun ce, ‘yan sanda da ma’aikatan kula da muhalli sun yi nasarar kama namun dajin daga baya kuma sun mayar da su kejin na su ba tare da sun raunata su ba.
Gidan kula da namun dajin na Arak na cikin mafi girma a kasar Iran.