fidelitybank

Zaben Shugaban Kasa: Libiya ta dakatar da zaben kada’a kuri’u

Date:

Majalisar dokokin Libya a ranar Litinin ta dage kada kuri’a kan yadda za a tunkari matsalar dage zaben kasar da aka yi, bayan wani zaman rudani da ke nuna rikicin siyasa kan makomar shirin samar da zaman lafiya.

A ranar Juma’a ne dai za a gudanar da zaben a matsayin wani bangare na yunkurin kawo karshen rikice-rikice da tashe-tashen hankula da aka kwashe shekaru goma ana yi a kasar Libiya ta hanyar kafa sabon shugaban kasa da majalisar dokokin kasar da ke da hakki na kasa, sai dai an dage zaben bayan takaddama kan dokokin.

Tuni dai ‘yan takara da kungiyoyin siyasa da ‘yan siyasa ke ta cece-kuce kan tsawon lokacin da ya kamata a jinkirta zaben da kuma ko gwamnatin rikon kwarya ta gwamnatin hadin kan kasa ta Firayim Minista Abdulhamid al-Dbeibah za ta iya ci gaba a halin yanzu.

Zaman majalisar na ranar litinin ya kasance mafi girma tun bayan da aka kafa gwamnatin Dbeibah a watan Maris, kuma shi ne na farko tun lokacin da aka hada ‘yan majalisa daga dukkan bangarorin da ke rikici da juna a zauren majalisar.

A makon da ya gabata ne dai hukumar zaben kasar Libiya ta bayyana cewa ba za a iya gudanar da zaben ba, saboda abin da ta kira gazawa a cikin dokokin zabe da kuma tsarin daukaka kara na shari’a tare da bayar da shawarar jinkirta zaben zuwa ranar 24 ga watan Janairu.

latest news in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...

Tinubu ya haramta fitar da ɗanyen man kaɗanya

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin dakatar...

Hisba ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 83,776 a Kano

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa, a...

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...

An gargadi Borno da Yobe da Jigawa su zama cikin shirin ambaliya

Akwai yiwuwar samun ambaliya a jihohin Borno, Jigawa da...
X whatsapp