fidelitybank

Zaben Kashim Shettima a matsayin mataimakin Sanata Bola Ahmed Tinubu yin Allah – Adamu

Date:

Shugaban jam’iyyar APC, mai mulki, Sanata Abdullahi Adamu, ya shawarci mabiya addinin Kirista da su daina wata fargaba a kan tsayar da dantakarar shugaban kasa na 2023, Musulmi da mataimakinsa Musulmi da jam’iyyar ta yi.

Shugaban ya ce yanayin halin da siyasar kasar ke ciki ne a yanzu ya janyo hakan, wanda idan har jam’iyyar na son ta ci zaben 2023 sai ta yi hakan, amma ba abu ne da wani zai so ba a ce an yi wannan tsari.

Sanata Adamu, ya ce, zaben Kashim Shettima a matsayin mataimakin Sanata Bola Ahmed Tinubu, abu ne yin Allah.

Da yake yi wa manema labarai bayani bayan wata ganawa ta sirri da Shugaban kasar Muhammadu Buhari, a Daura, Jihar Katsina a jiya Laraba, tsohon gwamnan na Nassarawa, ya ce bai kamata wannan zabi ya zama abin korafi ba ga al’ummar Kirista.

Ya ce: ”Gaskiyar lamari ita ce, ba abin da Allah Yake yi haka kawai. Allah Yana da dalilinsa na samar da manyan addinai biyu a kasar nan, kuma kowanne daga cikinsu, yana da mutanen da suke da dalilin binsa kuma suna hakki suma.”

”Akwai lokacin da Kirista ke jagorantar kasar nan. Yanzu kuma lokaci ne da Musulmi ke shugabantar kasar, ba za mu musanta wanna ba. Ba za mu iya samun lalle abin da muke so ba a wani lokaci, a ce dukkanin mu, mun amince da abu daya,” in ji shi.

Ya kuma kara da bayanin cewa, ” Ba lalle ba ne sai dukkaninmu mun kasance Musulmi ba ko kiristoci. Nufi ne na Allah a wannan lokacin cewa Shettima zai kasance mataimakin shugaban wannan babbar kasa, idan muka ci zabe. Abin da muke fata da kuma addu’a, wanda kuma muna kokarin cin zaben.”

spw

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu É—auki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta É—aukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...

Duk wasu Æ™awayen Amurka za su É—anÉ—anar kuÉ—arsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...

Iran ta mayar da martani kan sojojin Amurka dake Qatar

Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayyana cewa ƙasar ta...

Faransa ba ta goyon bayan Amurka na kifer da gwamnatin Iran – Barrot

Ministan harkokin wajen Faransa ya ce, ƙasarsu ba ta...

Kotu a Kano ta É—aure masu satar Yara

Babbar kotun jihar Kano da ke zamanta a Miller...

Ba wata hujja da Amurka za ta kai wa Iran hari – Rasha

An gudanar da tattaunawa tsakanin shugaban Rasha Vladimir Putin...

Tinubu ya miÆ™a saÆ™on ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...
X whatsapp