Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) a ranar Alhamis ta ce, ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da yin kira da kuma tayar da hankali a wasu sassan jihar Kano da gangan.
Jami’in hulda da jama’a na hukumar ta DSS, Peter Afunanya ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Abuja.
Afunanya ya ce wadanda ake zargin sun nadi sakonni daban-daban tare da yada su ta kafafen sada zumunta daban-daban.
Karanta Wannan: DSS ta cafke jigo a PDP bayan yukurin yin kisan kai
A wani bangare sanarwar ta kara da cewa, “A cikin wadancan sakonnin da za su iya cutar da su, sun dauki nauyin wasu muradun siyasa kuma sun yi kira ga magoya bayansu da su kai wa masu adawa da su hari da karfi.
“Wadanda ake zargin sun kuma yi kira da a kai wa jami’an tsaro hari yayin zaben gwamnoni da na ‘yan majalisar dokoki na ranar Asabar a jihar.
“Hukumar DSS ba za ta zuba ido tana kallon bata gari ko kungiyoyi suna zagon kasa ga zaman lafiya da tsaron jihar ba.”