fidelitybank

Zaben fidda gwani: A shirye muke mu bayar da ɗantakara a cikin mu – Bukola

Date:

Tsohon shugaban majalisar dattawa, Dakta Bukola Saraki, ya bayyana cewa dukkan masu neman takarar shugabancin kasa a jam’iyyar PDP daga yankin Arewa a shirye suke su bayar da dan takara a zaben fidda gwani na jam’iyyar ba tare da wata matsala ba.

Bukola ya bayar da wannan tabbacin ne a Bauchi a ranar Lahadin da ta gabata a lokacin da Saraki da Gwamna Aminu Tambuwal na jihar Sokoto, wanda kuma mai fatan zama shugaban kasa a jam’iyyar PDP, suka kai ziyarar tuntubar Gwamna Bala Mohammed na jihar Bauchi.

Saraki, wanda ya yi magana da manema labarai a madadin ‘yan takarar shugaban kasa uku, ya ce, sun ga ya zama wajibi a matsayinsu na masu ruwa da tsaki na jam’iyyar su gana, su yi tunani, domin ganin yadda abubuwa za su daidaita a tsakaninsu. Ya ce: “A yin haka, mun gana, muka tattauna cewa a nan gaba 2023, hadin kai da zaman lafiyar kasar nan da ci gaban kasa ya fi burin mutum daya muhimmanci. Mun kuma hadu domin yin kokari wajen ganin mun yi aiki tare.

Ya kuma ce, “Mun yi imanin cewa mu ukun muna yin aiki tare cikin jituwa, jajircewa da kuzari, za a sami babban fata ga kasar nan.

“Mun yaba da cewa mu ukun mun nuna muradin shugabancin kasar nan, amma kuma mun fahimci cewa, dukkanmu za mu iya, masu cancanta da kuma cancantar shugabancin kasar nan.

“A karshen wannan rana, mutum daya ne kawai zai jagoranci kasar nan a 2023; mun kuma yanke shawarar cewa, za mu yi aiki kafada da kafada ,domin ganin mun fito da hanyar da tsarin yarjejeniya zai zo tsakanin mu uku kan yadda za mu ci gaba da jagorantar kasar nan.”

Tsohon gwamnan na Kwara, ya bukaci daukacin magoya bayan jam’iyyar PDP da su mayar da hankali da hadin kai, domin daukaka jam’iyyar zuwa ga wani matsayi.

leadership newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp