fidelitybank

Zaben fidda gwani: A shirye muke mu bayar da ɗantakara a cikin mu – Bukola

Date:

Tsohon shugaban majalisar dattawa, Dakta Bukola Saraki, ya bayyana cewa dukkan masu neman takarar shugabancin kasa a jam’iyyar PDP daga yankin Arewa a shirye suke su bayar da dan takara a zaben fidda gwani na jam’iyyar ba tare da wata matsala ba.

Bukola ya bayar da wannan tabbacin ne a Bauchi a ranar Lahadin da ta gabata a lokacin da Saraki da Gwamna Aminu Tambuwal na jihar Sokoto, wanda kuma mai fatan zama shugaban kasa a jam’iyyar PDP, suka kai ziyarar tuntubar Gwamna Bala Mohammed na jihar Bauchi.

Saraki, wanda ya yi magana da manema labarai a madadin ‘yan takarar shugaban kasa uku, ya ce, sun ga ya zama wajibi a matsayinsu na masu ruwa da tsaki na jam’iyyar su gana, su yi tunani, domin ganin yadda abubuwa za su daidaita a tsakaninsu. Ya ce: “A yin haka, mun gana, muka tattauna cewa a nan gaba 2023, hadin kai da zaman lafiyar kasar nan da ci gaban kasa ya fi burin mutum daya muhimmanci. Mun kuma hadu domin yin kokari wajen ganin mun yi aiki tare.

Ya kuma ce, “Mun yi imanin cewa mu ukun muna yin aiki tare cikin jituwa, jajircewa da kuzari, za a sami babban fata ga kasar nan.

“Mun yaba da cewa mu ukun mun nuna muradin shugabancin kasar nan, amma kuma mun fahimci cewa, dukkanmu za mu iya, masu cancanta da kuma cancantar shugabancin kasar nan.

“A karshen wannan rana, mutum daya ne kawai zai jagoranci kasar nan a 2023; mun kuma yanke shawarar cewa, za mu yi aiki kafada da kafada ,domin ganin mun fito da hanyar da tsarin yarjejeniya zai zo tsakanin mu uku kan yadda za mu ci gaba da jagorantar kasar nan.”

Tsohon gwamnan na Kwara, ya bukaci daukacin magoya bayan jam’iyyar PDP da su mayar da hankali da hadin kai, domin daukaka jam’iyyar zuwa ga wani matsayi.

current eggon news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp