Jami’an hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa EFCC sun cafke akalla mutane uku da ake zargi da sayan kuri’u a zaben gwamna da ke gudana a jihar Edo.
Kamar yadda gidan talabijin na Channels ta ruwaito, an kama wadanda ake zargin ne a karamar hukumar Egor da ke jihar da misalin karfe 10:00 na safiyar ranar Asabar.
Jami’an EFCC sun bar wurin da mutane uku – maza biyu da mace daya.
Sai dai wasu mazauna garin sun nuna adawa da kama wadanda ake zargin, inda suka dage cewa ana cin zarafin wadanda ake zargin.
Hukumar ta yi gargadin cewa kafin zaben, ta gargadi jam’iyyun siyasa kan sayen kuri’u.