fidelitybank

Zaben 2023: PDP na yi wa Atiku hannunka mai sanda

Date:

Rahotanni na nuni da cewa, watakil Atiku Abubakar ya rasa tikitin takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP a 2023.

Wani babban jagora a jam’iyyar hamayyar ya ce, zai yi wahala a ce PDP ta sake tsayar da Atiku.

A halin yanzu Gwamnonin PDP masu ci sun sha gaban kowa a jam’iyya, kuma ba sa tare da Atiku.

Wani babba a jam’iyyar hamayya ta PDP, ya ce, da kamar wuya Atiku Abubakar ya rike tutar jam’iyya a zaben shugaban kasa da za ayi a 2023.

A ranar Talata, 8 ga watan Fubrairu 2022, jaridar Vanguard ta rawaito cewa, wannan jigo na jam’iyya ya na cewa gwamnonin PDP su na kara karfi a jam’iyya.

A hirar da aka yi da wannan tsohon gwamna na yankin Arewa maso yamma, ya bayyana cewa gwamnoni ne su ke rike da PDP, kuma sai yadda suka yi.

Ya ce.”Zai yi wahala Atiku ko waninsa ya iya doke wadannan gwamnoni masu ci a zaben fitar da gwani. Ana yi masa hannunka mai sanda, gwamnonin jihohi biyu sun fadawa Atiku gaskiya a ‘yan kwanakin nan, su na nuna masa ya hakura da 2023″. A cewarsa.

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed shi ma ya fito gar-da-gar ya na cewa, Atiku Abubakar ya na gaba da su a siyasa, kuma ya cancanta da mulki amma ya tsufa.

www.legit.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp