Tsohon shugaban majalisar dattawa Bukola Saraki, ya yanki tikitin sa na jamâiyyar PDP, domin tsayawa takarar shugaban kasa a babban zaben da ake sa ran zai yi a 2023.
Daily Independent ta ruwaito a ranar Litinin din da ta gabata cewa, kungiyar matasa kwararru a Najeriya sun tara Naira miliyan 40, domin siyan fom ga dan takarar shugaban kasa a zaben 2023.
Da ya ke mayar da martani kan lamarin, Saraki ya bayyana cewa, idan ya zama shugaban kasa a 2023, zai nada ministocin da ba su kai shekara 35 ba a tafiyar sa.
A cewarsa, shirin ya yi daidai da tafiyar sa ya dade yana ganin cewa, matasa na da dimbin gudunmawar da za su taimaka wajen ci gaban Najeriya.
Da yake jawabi jim kadan bayan karbar fom din tsayawa takara, Saraki ya ce, âDa wannan mataki da ka dauka a yau, ba ni da wani zabi illa in saurari muryar matasan da ke wakiltar kashi 62 cikin 100 na âyan Nijeriya sama da miliyan 200.
âDon haka ne nake so in yi alkawarin cewa idan na zama shugaban Najeriya, duk mukaman ministocin gwamnati a majalisar ministoci matasa ne za su mamaye su.
âWannan alkawari ne da ba zan yi kasa a gwiwa ba, domin na yi imanin cewa ana bukatar raâayoyin matasa don ciyar da ayyukan ci gaban zamani.
âAn gaya min cewa a wajen siyan fom din, da yawa daga cikin ku sun ba da gudummawar Naira 200,000, Naira 500,000 kuma mafi girma shi ne Naira miliyan 2. Wannan yunĈuri da ĈoĈari nagari watakila ba a taÉa yin irinsa ba a tarihin siyasar Nijeriya.