Babban Darekta Janar na hukumar yi wa ƙasa hidima, Birgediya-Janar Yusha’u Ahmed, ya ce, ‘yan bautar ƙasa 200,000 ne hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ɗauka a matsayin ma’aikatan wucin gadi waɗanda za su gudanar da aikin zaɓe.
Ahmed ya bayyana hakan ne a wani taron manema labarai a Abuja, inda ya yi kira ga ‘yan yi wa ƙasa hidiman da su lura da wuraren da za a aike su don yin aikin zaɓe.
Karanta Wannan: A kasa a tsare a raka ba zai yi aiki ba a zaben bana – INEC
Ya kuma gargaɗe su a kan karɓar kyauta daga wajen ‘yan siyasa.
“Bai kamata ‘yan yi wa ƙasa hidima su karɓi kyauta ba ta kowace iri, kawai su tabbatar sun gudanar da aikin da ya kai su,” in ji Ahmed.
Ya ce sun tattauna da sufeto janar na ‘yan sandan Najeriya da kuma hukumar tsaro ta farin kaya wajen ganin a bai wa masu yi wa ƙasa hidimar tsaro da ta kamata.