Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana cewa, nan gaba kadan zai bayyana kudurinsa na tsayawa takarar shugabancin kasar nan a 2023.
Atiku ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da manema labarai a birnin Minna na jihar Neja, jim kada bayan ya yi wata ganawar sirri da shugaban kasa na mulkin soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, a gidan sa na tudu na kusan sa’a daya.
Ya ce, burinsa na shugaban kasa a zaben 2023, idan lokaci ya yi zai fito fili ya bayyana.
Hakazalika, Atiku ya kuma kai ziyarar ban girma ga gwamnan Jihar Neja Alhaji Abubakar Sani Bello, domin jajanta masa kan karuwar kalubalen tsaro a jihar.