Gabanin zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya da za a yi a ranar 25 ga watan Fabrairu, hukumar shige da fice ta kasa ta sake tura kwanturolan jihohi 30 da mataimakan kwanturola Janar 11 a fadin kasar.
Wadanda sauyin ya shafa sun hada da mataimakan Kwanturola Janar 11 da ke kula da shiyyoyi daban-daban da kuma Kwanturola 30 da aka tura zuwa sabbin jihohi.
An bayyana hakan ne a wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar shige da fice, Tony Akuneme ya fitar.
A cewar mai magana da yawun NIS, jihohin da abin ya shafa sun fi wadanda suka yi iyaka da Najeriya da kasashe makwabta – Yobe, Adamawa, Sokoto, Katsina, Zamfara, Oyo, Lagos (Seme Border) da kuma Cross River.
Sauran jihohin da suke samun sabbin Kwanturola sun hada da Gombe, Kaduna, Kano, Plateau, Bauchi, FCT, Nasarawa, Edo, Bayelsa, Rivers (Marine Command), Anambra da Enugu, da dai sauransu.
Bukatar da Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa, Isah Jere Idris ya amince da shi, ya samu sa hannun Mataimakin Kwanturolan Janar (Human Rights), Usman Babangida.
Da yake lura da cewa dukkan dakarun na tare da gaggawa, kakakin NIS ya ce hukumar ta CGIS ta ba da fifiko sosai kan muhimmiyar rawar da jami’anta ke takawa wajen samun nasarar babban zaben.