Kwamitin ayyuka na jam’iyyar All Progressives Grand Alliance (APGA), ya kaddamar da shirin gudanar da zabukan 2023 wanda ya fara da sayar da fom din tsayawa takara da kuma nuna sha’awa da aka shirya farawa a ranar Talata mai zuwa.
A cewar wata sanarwa da jam’iyyar APGA ta fitar, kuma aka rabawa manema labarai ranar Juma’a a Abuja, za’a fara siyar da fom na nuna sha’awa da kuma dawo da fom din takara daga ranar 29 ga Maris da 11 ga Afrilu, 2022 Sakatariyar APGA ta kasa, Abuja.
Har ila yau, ta sanar da cewa, za a gudanar da tantance ‘yan takarar majalisar dokokin kasar ne tsakanin 20 da 21 ga Afrilu, 2022, yayin da ake tantance masu neman takarar shugaban kasa da na Gwamna – 22 – 23 ga Afrilu, 2022.
Jam’iyyar ta kuma yi nuni da cewa, ‘yan takarar mata da masu fama da nakasa za su biya kashi 50% na kudaden da aka tanada a sama na duka fom na nuna sha’awa da na takara.
A halin da ake ciki, shugabannin jam’iyyar APGA sun yi jinjina ga tsohon gwamnan jihar Anambra, Cif Willy Obiano bisa ayyukan da ba a saba gani ba a cikin shekaru takwas na gwamnatinsa a jihar.